![]( /mmsource/images/2006/03/22/afirkaayau2.jpg)
Lokacin da manema labaru suka yi mata tambayoyi game da wannan, madam Johnson-Sirleaf ta ki bayar da amsa, ta ce, ta yi imani cewa, za a gabatar da sakamakon karshen cikin adalci. Idan mutanen kasar Liberia suna goyon bayanta, sun gaskata da ita, to, za ta yi musu ayyuka, za ta kawo musu zaman lafiya, za ta rage musu wahaloli, a matsayin shugaban kasar.
Ko da yake an sa aya ga yakin basasa a shekarar 2003, amma ba a samu hadin gwiwa tsakanin jam'iyyu da rukunnoni dabab daban ba, game da wannan kuma, madma Johnson-Sirleaf ta yi bayani cewa, mutanen kasar Liberia suna da burinsu, sun san mene ne za su yi da yadda za su yi.
Yanzu tana fuskantar nasara, amma madma Johnson-Sirleaf ba ta nuna girman kai ba, a maimakon haka ta san babban nauyin da aka danka mata bisa wuyanta, ta riga ta fara yin tunanin yadda za a canja odar zaman al'ummar kasar Liberia maras kwanciyar hankali. 1 2 3
|