Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-02-23 18:21:41    
Yin rigakafi da shawo kan cutar murar tsuntsaye ya zama muhimmin aiki na kasar da kasa musamman na Afirka

cri

A ran 21 ga wata, ministar kiwon lafiya ta kasar Zambia ta bayyana a gun wani taron majalisar dokoki ta kasar cewa, gwamnatin kasar Zambia ta riga ta kebe kudin da yawansu ya kai dala miliyan 4 da dubu 850 domin shawo kan cutar murar tsuntsaye da mai yiwuwa ne za ta bulla a kasar. Ta ci gaba da cewa, za a yi amfani da wannan kudi ne a kan farfagandar yin rigakafin cutar murar tsuntsaye, ban da wannan kuma, za a bayar da kudin ga mutane da suke kiwon tsuntsayen gida amma aka kashe tsuntsayensu a sakamakon cutar.

A ran 22 ga wata, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Ukraine ta bayar da wata sanarwar cewa, a 'yan kwanakin baya, tsuntsayen gida masu yawan gaske sun mutu a kauyuka biyu da ke kudancin kasar. A halin yanzu, ana bincike da nazarin tsuntsayen da suka mutu, haka kuma ana kashe kwayoyin cuta a kauyukan biyu.


1  2  3