
Lokacin tun daga yanzu zuwa babba zaben da za a yi a ran 30 ga watan nan bai kai kwaniki 20 ba, amma farmakinn tashin hankali da kisan gilla da kuma yin garkuwa suna yi ta karuwa. Bisa labarin ran 12 ga wata na "Jaridar Dala", a cikin wannan mawuyacin hali, ministan harkokin waje na gwamnatin wucin gadi na kasar Iraki Hoshyar Zebari ya ce, wannan "babban zabe ba zai kauce wa laifufuka, kuma ba za a iya tafiyar da babban zabe cikin zaman lafiya". Kafin wannan kuma, firayin ministan gwamnatin wucin gadi Iyad Allawi ya taba yarda da cewa, saboda halin da ake ciki na yanzu a wasu wuraren kasar Iraki ba za a iya tabattar da zaman lafiyar masu jefa kuri'a.
Mr.Hoshyar Zebari ya ce, akwai larduna 14 cikin duk lardun 18 na kasar za a iya tafiyar da babban zabe cikin lafiya, amma sauran larduna 4 akwai matsaloli. Ko da yake haka, kamar ra'ayin Iyad Allawi, Mr.Zebari yana tsammani bai kamata a daga babban zabe ba.
1 2 3
|