Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An zabi kasar Sin a matsayin mambar hukumar kare hakkin dan adam daga 2021-2023
2020-10-14 10:21:08        cri
An zabi kasar Sin a matsayin mambar hukumar kare hakkin dan Adam, daga shekarar 2021-2023, a zaben da aka yi jiya, a babban zauren MDD karo na 75.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Sin dake MDD ya fitar, ta ce Sin na godiya matuka ga kasashe mamabobin majalisar, saboda goyon bayan da suke bata, sannan ta taya sauran mambobin da aka zaba murna.

Hukumar wadda aka kafa a 2006, hukuma ce mai mambobi 47 dake karkashin MDD, wadda ke da nauyin kare hakkin dan adam. Babban zauren MDD ne ke zabar mambobin hukumar, sai dai ba za su iya yin tarce fiye da sau daya ba, sai dai bayan wani lokaci a sake zabensu.

An zabi kasar Sin a matsayin mambar hukumar har sau 5 wato a shekarar 2006 da 2009 da 2013 da 2016 da kuma 2020. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China