Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Gwamnatin Yankin Hongkong Ya Yi Maraba Da Dokar Tsaron Yankin
2020-06-30 20:26:12        cri
Kantonmar yankin Hongkong Carrie Lam, ta ba da wata sanarwa game da dokar tsaron yankin musamman na Hongkong, wadda zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya zartas a yau Talata.

A cikin sanarwar, jami'ar ta nuna cewa, kiyaye tsaron kasar nauyi ne dake wuyan yankin Hongkong, kuma gwamnatin yankin na maraba da wannan doka da kwamitin ya zartas a yau.

Ban da wannan kuma, ta ce gwamnatinta za ta kafa kwamitin kiyaye tsaron kasar, karkashin shugabancinta, bisa tanade-tanaden wannan doka ba tare da bata lokaci ba.

A hannu guda kuma, hukumar 'yan sanda, da sashin doka da shari'a, za su kafa hukuma ta musamman, don aiwatar da ayoyin dake kunshe cikin wannan doka. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China