![]() |
|
2020-05-29 12:49:49 cri |
A cewar gwamnan babban bankin kasar, Godwin Emefiele, hada hadar tattalin arzikin 'yan Najeriya ta tsaya cik a yayin da ake yaki da cutar a kasar. Yana kyautata tsammanin za'a iya samun raguwar karfin tattalin arzikin kasar a cikin rubu'i na biyu na wannan shekarar da muka ciki.
Gwamnan ya fadawa 'yan jaridu cewa, Najeriya wani muhimmin ginshiki ne a tattalin arzikin duniya. Idan har kasar za ta iya jurewa wannan yanayi da ake ciki game da tasirin annobar cikin kankanin lokaci, kana za ta hada kai da sauran kasashen duniya domin fita daga matsanancin halin da ake ciki, hakika da hakan zai fi dacewa ga kasar.
Ya jaddada bukatar yin aiki tare domin cimma nasarar bunkasuwar tattalin arziki.(AHMAD)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China