![]() |
|
2020-05-14 12:59:21 cri |
Wata majiya ta jami'an sojin Najeriyar ce ta tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua. Majiyar ta kuma ce galibin mutanen da sojojin suka kubutar mata ne da kananan yara.
Sojojin dai sun kaddamar da jerin hare hare ne kan sansanonin mayakan na Boko Haram, tun daga ranar 4 ga watan nan na Mayu. Majiyar ta kara da cewa, yayin wannan samame, an hallaka a kalla mayakan kungiyar 18, yayin da kuma wasu da dama suka tsere da harbin bindiga.
Bugu da kari, sojojin sun kwato tarin makamai da harsasai, da kayayyakin fada, da sauran na'urori da 'yan ta'addan na Boko Haram ke amfani da su. An kuma kama wasu masu agazawa kungiyar. (SAMINU)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China