Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Mutane sama da 13000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a nahiyar Afrika
2020-04-13 12:28:03        cri
Cutar numfashi ta COVID-19 na ci gaba da yaduwa a nahiyar Afrika, inda ya zuwa yammacin ranar Asabar, aka tabbatar mutane sama da 13000 sun harbu, yayin da 744 suka mutu sanadiyyar cutar.

A kokarinta na tunkarar tasirin annobar kan tattalin arziki, Tarayyar Afrika (AU) ta nada wasu wakilai na musammam da za su kula da batun tallafin kasashen duniya ga nahiyar.

Ana ganin akwai yiyuwar tsarukan kiwon lafiya a nahiyar da suka tabarbare za su ci gaba da fuskantar gagagrumar matsala, musammam a yankunan karkara. A don haka, hukumar lafiya ta duniya ta yi kira ga kasashen Afrika su dauki matakan gaggawa na karfafa tsarukan kiwon lafiyar al'umma da na kiwon lafiya a matakin farko, inda kuma ta yi kira ga kungiyar G20 ta gaggauta tallafawa nahiyar a kokarinta na yaki da cutar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China