![]() |
|
2020-04-03 10:13:00 cri |
Ya yi wannan tsokaci ne a lokacin da yake ganawa da jakadan kasar Sin a AU, Liu Yuxi, wanda ya gudana a helkwatar kungiyar ta AU dake Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.
A wata sanarwa da Quartey ya wallafa a shafinsa na Facebook ya ce, sun tattauna ne game da yadda za'a kara yin hadin gwiwa da zurfafa cudanya tsakanin kungiyar AU da kasar Sin wajen yakar annobar COVID-19 a Afrika.
Taron bangarorin biyu yana daga cikin kokarin da hukumar gudanarwar AU take yi da nufin dakile annobar ta COVID-19, da nufin zurfafa hadin gwiwa tsakanin AU da kasar Sin don kawar da cutar COVID-19 a Afrika, karkashin dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu. (Ahmad)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China