![]() |
|
2020-03-26 20:49:28 cri |
Cibiyar ta CDC, wadda ta bayyana hakan cikin alkaluman da take fitarwa, ta ce kasashen Afirka 16, sun tabbatar da rasuwar mutane 72 bayan fama da cutar ta COVID-19.
Kasashen da annobar cutar ta fi kamari dai sun hada da Afirka ta Kudu mai mutane 709, da Masar mai mutum 456, da Algeria mai 302, sai kuma kasar Morocco mai mutane 225.
Cikin jimillar wadanda cutar ta harba a nahiyar Afirka, cibiyar ta CDC ta ce akwai mutane 210, daga kasashe 14 da tuni suka warke bayan samun kulawar jami'an lafiya.(Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China