![]() |
|
2020-03-14 20:28:11 cri |
A karkashin irin wannan yanayi, kafofin watsa labaran kasashen yamma wadanda suka taba sukar kokarin da kasar Sin take na yakar annobar su ma sun amince cewa, kasashen duniya sun bata lokaci mai dajara da kasar Sin ta samar musu, kuma idan ba su himmantu ba, tattalin arzikin duniya zai dagule sanadin tasirin annobar.
Har kullum kasar Sin tana daukar hakikanin matakai domin yaki da annobar tare da sauran kasashe, alal misali ta kafa kungiyar kwararru cikin hadin gwiwa da kasashen Turai, ta kuma samar da tallafin kayayyakin kiwon lafiya cikin gaggawa ga kasashe da dama da suke bukata, kana ta tura kwararrun da abin ya shafa zuwa kasashen Iran da Iraki da Italiya da sauransu domin yaki da annobar tare, ban da haka, gwamnatin kasar Sin ta samar da tallafin kudi dalar Amurka miliyan 20 ga hukumar lafiya ta duniya domin taimakawa kasashe masu tasowa a bangaren. Duk wadannan matakan da kasar Sin ta dauka sun samu jinjina daga MDD da hukumar lafiya ta WHO. A jiya, shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa, alkaluma da bayanan da kasar Sin ta samar wa kasarsa za su taimaka mata matuka, shi ma ya amince cewa, kasar Sin ta samu sakamako a bayyane kan aikin dakile annobar.
Annoba tana shafar daukacin kasashen duniya, idan ana son cimma burin ganin bayanta, dole ne kasashen duniya su hada kai cikin hanzari.(Jamila)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China