![]() |
|
2020-02-04 19:35:56 cri |
Madam Hua ta kara da cewa, hukumar WHO ta sanar a ranar 3 ga wata cewa, ban da kasar Sin, akwai mutane 153 da aka tabbatar da suka kamu da annobar cutar numfashi a wasu sassan duniya, wadanda yawansu bai kai kaso 1 cikin dari na jimillar wadanda aka tabbatar da suka kamu da cutar a kasar Sin ba. A shekarar 2009, annobar cutar murar H1N1 da ta barke a kasar Amurka ta yadu a duk duniya har da kasashe da yankuna 214. Sakamakon kokarin da kasar Sin take yi, ya sa annobar cutar numfashi ba ta yadu zuwa sauran kasashe ba. Hukumar WHO ta yaba wa matakan da kasar Sin ta dauka a matsayin sabon abin koyi a fannin yaki da barkewar annobar cuta. Kasar Sin ta fahimci matakan da wasu kasashe suka dauka domin hana yaduwar annobar, amma ta yi fatan cewa, za su kara daukar matakai yadda ya kamata, a magance dakatar da zirga-zirgar mutane. (Tasallah Yuan)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China