![]() |
|
2019-08-11 16:23:31 cri |
Ofishin watsa labarai na shugaban kasar ne ya gabatar da sanarwar a Dar es Salaam, cibiyar tattalin arziki ta kasar, an ce an fara zaman makokin ne tun daga jiya Asabar, kuma zai ci gaba har zuwa Litinin mai zuwa.
An kara bayyanawa a cikin sanarwar cewa, za a saukar da tutocin kasar dake wurare daban daban zuwa rabin sanda, yayin da ake zaman makokin, sa'an nan shugaba Magufuli zai tura firaministan kasar Kassim Majaliwa zuwa birnin Morogoro, domin ya halarci bikin jana'izar wadanda suka rasu, a madadin shugaban kasar.
A daren jiya, 'yan sandan kasar sun ce yawan mutanen da suka mutu ya karu zuwa 64, sakamakon fashewar tankar mai a Morogoro, dake da nisan kilomita 200 a yammacin birnin Dar es Salaam. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China