Shugaba Xi zai kai ziyara Koriya ta Arewa
Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin koli na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping, zai gudanar da ziyarar aiki a kasar Koriya ta Arewa, tsakanin ranekun 20 zuwa 21 ga watan nan na Yuni, bisa gayyatar shugaban Koriya a Arewa Kim Jong Un, wanda shi ne jagoran jami'iyyar "Workers' Party", kuma shugaban hukumar zartaswar Koriya ta Arewa. (Saminu Alhassan)
Labarai masu Nasaba