![]() |
|
2020-10-09 21:07:22 cri |
A kalla mutane 8 ne aka tabbatar sun rasu, yayin gobarar iskar gas din da ta auku a jiya Alhamis, a wani gidan mai dake unguwar Baruwa, wadda ke wajen birnin na Lagos cibiyar kasuwancin kasar.
A yau Juma'a, gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu, ya fitar da wata sanarwa, dake nuna matukar kaduwarsa bisa aukuwar gobara, wadda ta hallaka mutane da barnata dukiyoyi, al'amarin da ya ce ya yi matukar bakantawa gwamnatin sa rai.
Gwamnan ya ce rahotannin farko da aka samar, sun nuna cewa, akwai sakacin aiki a bangaren mahukuntan gidan man, wanda hakan ya sabbaba tashin gobarar. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China