![]() |
|
2020-10-08 16:30:33 cri |
Mutanen sun hada da 'yan kasar Rasha uku, da dan kasar Ukraine, sai guda dan kasar Equatorial Guinea, sojojin sun yi nasarar kubutar da mutanen ne yayin samamen da suka kaddamar a maboyar 'yan bindigar, John Enenche, kakakin rundunar tsaron Najeriyar ne ya bayyana cikin wata sanarwa.
Enenche ya ce, wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi garkuwa da ma'aikatan 'yan kasashen waje tun a ranar 9 ga watan Mayun shekarar 2020.
Bakin da aka kubutar suna samun kulawar likitoci a wani asibitin sojoji, kamar yadda Enenche ya bayyana.(Ahmad)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China