Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta biyan dukkan kudadenta na karo-karon MDD na wannan shekara
2020-09-04 20:10:15        cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Hua Chunying, ta bayyana a Jumma'ar nan cewa, a matsayinta na kasa ta biyu da ke ba da kaso mafi yawa ga MDD, kasar Sin ta biya dukkan kudaden karo-karon da ya kamata ta biya a wannan shekara, abin da ke nuna irin gudummawar da kasar ta Sin ke baiwa MDD.

Madam Hua ta ce, kasar Sin za ta ci gaba da sauke nauyin dake bisa wuyanta wajen biyan kudaden karo-karo da ya kamata ta baiwa MDD a matsayinta na kasa mai tasowa.

Rahotanni na cewa, a kwanakin nan, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya aikawa kasashe mambobin majalisar wasika, yana mai kira a gare su, da su biya kudaden ya kamata su biya a kan lokaci don taimakawa MDD kammala ayyukanta a wannan shekara. (Ibrahim Yaya)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China