Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga 3 a arewa maso yammacin kasar
2020-08-22 17:10:27        cri
Rundunar sojojin Najeriya ta tabbatar da kashe 'yan bindiga 3 da kuma damke wasu 10 a samamen da ta kai na baya bayan nan a shiyyar arewa maso yammacin kasar mai fama da rikici.

A wata sanarwa da aka baiwa kwafenta ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Juma'a, hukumar sojojin ta ce ta kaddamar da aikin samar da tsaron ne a ranar Lahadi a wasu yankuna dake dajin Dumburum, inda ake zargin barayin suna samun mafaka.

Sojojin sun kashe 'yan bindigar uku a cikin dajin, kana sun kama wasu mutanen 10 da ake zargi a shirin murkushe 'yan bindigar a jahohin Katsina da Zamfara, da sauran yankunan shiyyar arewa maso yammacin kasar, in ji kakakin rundunar sojojin kasar Benard Onyeuko.

A cewar Onyeuko, an gano wasu makamai da harsasai a lokacin samamen, wanda sojojin suka shafe kwanaki suna gudanarwa.

Ya kara da cewa, an yi nasarar kubutar da mutane 10 wadanda 'yan bindigar suka yi garkuwa dasu.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China