![]() |
|
2020-08-22 17:01:41 cri |
Xi, ya yi wannan tsokaci ne a yayin taron tattaunawa da aka gudanar a ranar Alhamis a Hefei, babban birnin lardin Anhui dake shiyyar gabashin kasar Sin.
Cikin jawabin da ya gabatar a lokacin taron, shugaba Xi ya ce, tsarin dunkulewar shiyyar da hadewar bangarorin kayayyakin more rayuwar jama'a sun taka muhimmiyar rawa a aikin kandagarki da yaki da annobar COVID-19 gami da farfadowar tattalin arziki.
Ya bukaci a samu fahimta mai zurfi game da matsayin yankin kogin da irin alfanun da yake da shi ga cigaban tattalin arzikin kasar Sin da zamantakewar alumma, domin a samu damar kara inganta dunkulewar bunkasuwar shiyyar a daidai lokacin da ake fama da yanayi na rashin tabbas.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China