![]() |
|
2020-08-20 20:48:21 cri |
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Borno Isa Gusau ya fitar, ta bayyana cewa, rundunar hadin gwiwar ta yi nasarar ceto mutanen, da suka hada da maza baligai 37 da mata baligai 17 da yara 40 ne, yayin wani musayar wuta da suka fafata da mayakan a yankin na tafkin Chadi.
Kwamishinan shari'a na jihar Borno, Kakashehu Lawal, wanda ya karbi mutanen da aka ceto, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, gwamanti za ta gudanar da bincike, da sake musu tunani, ta kuma hade wadanda ake ceton da iyalansu, ta yadda za su yi rayuwa kamar kowa.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China