![]() |
|
2020-08-18 14:56:41 cri |
A zantawarsa da Murtala Zhang, Abubakar Ayuba Isah ya bayyana cewa, yana jin dadin zaman rayuwa da karatu a nan kasar Sin, duk da cewa yanayin karatu tsakanin gida Najeriya da kasar Sin ya bambanta kwarai. Abubakar ya kara da cewa, farkon zuwansa kasar Sin, ya gamu da matsalolin abinci, amma yanzu ya saba da abincin kasar sosai.
Abubakar ya kara da cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu a fannin tattalin arziki da zaman rayuwa ya burge shi kwarai da gaske, abun da ya karfafa masa gwiwar kara neman ilimi domin bautawa kasarsa Najeriya. Ya kuma yi kira ga matasan Najeriya da su maida hankali kan muhimmancin ilimi, saboda a cewar malam Bahaushe, ilimi shi ne hasken rayuwa.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China