![]() |
|
2020-08-03 11:19:09 cri |
A ranar 31 ga watan Yuli ne, wakilan EU da jakadun kasashen Turai 15, suka aike da wasika ga ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila, inda suka bayyana adawarsu da matakin gwamnatin Isra'ilar na fara gini a yankin Givat Hamatos.
Hanan Ashrawi, mambar kwamitin zartarwa na kungiyar 'yantar da al'ummar Falasdinu, ta bukaci jami'an na Turai su dauki matakin da zai hana Isra'ila aiwatar da shirin nata.
Cikin wata sanarwa, Hanan Ashrawi ta ce sun yi ammana cewa, ya kamata Tarayyar Turai da gwamnatocin kasashe 15, su dauki matakan da za su hana Isra'ila ci gaba da ayyukan keta doka da cin zarafi da mamaya. (Faiza Mustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China