![]() |
|
2020-08-01 16:52:36 cri |
Kawo yanzu, wadannan sojoji masu aikin jinya na kasar Sin sun duba marasa lafiya da yawansu ya kai 2,944, da gudanar da ayyukan tiyata har sau 58. Bayan barkewar cutar COVID-19 a wurin da suke gudanar da aikin shimfida zaman lafiya a Mali, asibitin da sojojin Sin suka kafa ya zama asibiti daya kacal na tawagar shirin MINUSMA na MDD mai wanzar da zaman lafiya a Mali, wanda ke iya ci gaba da gudanar da ayyukan samar da magani ga marasa lafiya, al'amarin da ya shaida cewa, sojojin kasar Sin sojoji ne wadanda suka cancanci amincewa, har ma sun samu lambar karramawa daga tawagar ta MINUSMA saboda jajircewar da suka yi na ceton rayuka a wuraren da ake kiyaye zaman lafiya.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China