![]() |
|
2020-07-30 21:11:18 cri |
Kaza lika a yayin taron na yau, hukumar siyasa na kwamitin koli na JKS, ya duba halin da tattalin arzikin Sin ke ciki, tare da tsara aikin da za a gudanar a watanni 6 na karshen shekarar.
Ana sa ran yayin taron na watan Oktoba, hukumar siyasa ta kwamitin koli na JKS, za ta gabatar da rahoton aikin sa, lokacin da kuma mahalarta taron za su nazarci shawarwari da aka gabatar, game da tsarin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al'ummar kasar Sin na shekaru biyar biyar na 14, wanda za a aiwatar tsakanin shekarun 2021 zuwa 2025, da ma kudurin ci gaban kasar, na nan da shekarar 2035. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China