Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Pompeo ya kunyata kansa kan kalaman da yake a kan Xinjiang
2020-07-06 20:44:12        cri

Kwanan baya, gidan talabijin na CGTN dake karkashin babban gidan rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG a takaice, ya bullo da wani shirin TV, mai taken "tunawa da yadda ake kokarin dakile ta'addanci a jihar Xinjiang ta kasar Sin", wanda ya jawo hankalin masu kallo ta kafar intanet sosai. Daya daga cikinsu mai suna Francisca ta bayyana ra'ayinta cewa, kowace kasa tana da iko da nauyin dake wuyanta na yaki da masu tsattsauran ra'ayin addini da ayyukan ta'addanci, kuma idan ana son kawar da wadannan munanan abubuwa, ya zama dole a inganta aikin bada ilimi da samar da isassun ayyukan yi.

Kalaman Francisca sun shaida cewa, rigakafi ya fi magani a yayin da ake yakar ta'addanci. Idan ana son kawar da tushen ayyukan ta'addanci, akwai bukatar raya tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al'umma. Amma a tunanin sakataren harkokin wajen Amurka wato Mike Pompeo, ba haka lamarin yake ba, saboda kwanan nan, ya sake zargin kasar Sin cewa, wai ana tursasawa gami da kame dimbin fursunoni a jihar Xinjiang, a wani yunkuri na shafawa gwamnatin kasar kashin kaji kan kwararan matakan da ta dauka na yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi.

Hakikanin gaskiya, kalaman Pompeo ba su da tushe balle makama. Kamar yadda kasashen duniya da dama ke ganin cewa, batutuwan da suka jibanci jihar Xinjiang, ba batutuwa ne da suka shafi hakkin dan Adam ko wata kabila ko kuma wani addini ba, amma batutuwa ne da suka shafi yaki da ayyukan ta'addanci da masu yunkurin kawowa kasar Sin baraka. Domin daidaita wadannan matsaloli tun daga tushensu, gwamnatin kasar tana iyakacin kokarinta wajen inganta samar da ilimi da isassun ayyukan yi. Kuma shaidu sun nuna cewa, taimakawa 'yan kananan kabilu samun guraban ayyukan yi na daya daga cikin muhimman matakan da aka dauka domin tabbatar da hadin-kai da zaman lafiya gami da bunkasuwa a jihar ta Xinjiang.

A kwanan nan, akwai kasashe da dama wadanda suka sake jaddada goyon-bayansu ga manufofin gwamnatin kasar Sin kan jihar Xinjiang. Kuma 'yan kasashen waje da dama da suka taba kai ziyara jihar, sun nuna cewa, ayyukan yakar ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi da kasar Sin take gudanarwa, abubuwan koyi ne ga kasashen duniya.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China