Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Tawagar jami'an lafiyar Sin sun koma gida daga Zimbabwe da Equatorial Guinea
2020-06-23 09:53:03        cri

Wata tawagar jami'an kiwon lafiya wanda lardin Hunan da ke yankin tsakiyar kasar Sin ya zabe su sun riga sun koma gida bayan sun bada taimako a aikin yaki da annobar COVID-19 a kasashen Zimbabwe da Equatorial Guinea.

Hukumar lafiyar kasar Sin ne ta aike da tawagar kai tsaye zuwa kasar Zimbabwe tare da tallafin kayayyakin kiwon lafiya wanda gwamnatin lardin ta samar a ranar 11 ga watan Mayu, inda suka gudanar da aikin kula da lafiya a kasashen Afrika na tsawon wata guda.

Zhu Yimin, mataimakin daraktan hukumar lafiya na lardin Hunan, kana shugaban tawagar, ya ce sun ziyarci wasu cibiyoyin kiwon lafiya da na gwaje-gwaje a kasashen Zimbabwe da Equatorial Guinea domin yin musayar kwarewar da kasar Sin ta samu a yaki da annobar COVID-19.

A cewar Zhu, tawagar ta yi aikin hadin gwiwa da jami'an lafiyar kasashen game da aikin kula da majinyata da baiwa ma'aikatan lafiya na kasashen shawarwari dangane da aikin gwaje-gwaje domin inganta yanayin gwajin masu kamuwa da cutar. Tawagar ta kuma mika wasu rubutattun bayanan shawarwarin kwararru kan dabarun yin kandagarki da dakile yaduwar annobar. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China