Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga 135 a arewa maso yammacin kasar cikin kwanaki 3
2020-05-24 16:07:15        cri
A kalla 'yan bindiga 135 sojojin Najeriya suka kashe a jahohin Zamfara da Katsina dake shiyyar arewa maso yammacin kasar, kakakin sojojin Najeriya ne ya tabbatar da hakan a ranar Asabar.

John Enenche, mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriya ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikewa kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce an kashe 'yan bindigar ne a yayin wasu hare hare ta jiragen sama da rundunar musamman ta sojojin Najeriya ta Operation Hadarin Daji suka kaddamar a yankuna masu yawa a jahohin biyu tsakanin ranar Laraba zuwa Juma'a.

A cewar kakakin sojojin, hare haren ta sama na daga cikin sabbin munanan hare haren da sojojin suka kaddamar a shiyyar arewa maso yammacin Najeriyar da nufin murkushe ayyukan mayakan 'yan bindigar da sauran bata gari a yankunan.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China