2020-03-18 08:34:56 cri |
Malama Pianduo mai shekaru 37 ta zo ne daga birnin Shigatse na jihar Xizang ta kasar Sin. A shekarar 2014, an dauke ta aiki a gidan marayu da ke birnin Lhasa na jihar, inda ta zama "mama" ga yara 22. A wannan gidan marayu, akwai yara 300, wadanda suka rasa iyayensu, kuma wadanda aka karkasa su cikin gida 18, kowane gida kuma akwai wata "mama" da ke kula da su. A farkon shekarar 2015, malamar ta fara kula da yara 22 da ke cikin gida na 10, inda take zama tare da su da kuma kula da rayuwarsu.(Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China