Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Hu Chunhua ya bukaci a zage damtse don samun nasarar kawar da talauci a kasar Sin
2020-03-12 12:01:56        cri

Shugaban tawagar da ke aikin kawar da talauci da raya kasa na majalisar gudanarwar kasar Sin Hu Chunhua a jiya Laraba ya shugabanci cikakken zaman taron tawagar, inda ya jaddada cewa, kamata ya yi a kara himmatuwa wajen gudanar da ayyukan saukaka fatara da kawar da talauci a fadin kasar, kuma a yi kokarin saukaka illolin da cutar numfashi ta Covid-19 ke haifarwa ga ayyukan, ta yadda za a cimma burin da aka sanya gaba na kawar da talauci da kuma kafa al'umma mai wadata.

Hu ya jaddada cewa, kamata ya yi a kammala ayyukan kawar da talauci daga dukkan fannoni, kuma a sa ido kan yadda ake gudanar da ayyukan, ta yadda za a kai ga fitar da ragowar gundumomi da al'umma da ke fama da talauci gaba daya daga kangin da suke ciki. Baya ga haka, ya kamata a yi kokarin ganin wadanda aka fitar daga talauci, ba su kowawa ba, kuma a gaggauta kafa tsarin sa ido da na tallafa musu, ta yadda za a gano wadanda suke da matsalar da wuri da kuma samar musu tallafi da wurin. Baya ga haka, ya kamata a tallafa wa yankuna da al'ummar da ke fama da talauci ta hanyoyin bunkasa masana'antu da samar musu ayyukan yi da sauransu, kuma a tabbatar da samar musu da ilmin tilas da hidimomin kiwon lafiya da gidajen kwana da ruwan sha. Daga karshe, ya jaddada cewa, ya kamata a saukaka illolin da cutar Covid-19 ke haddasawa, kuma a gaggauta aiwatar da matakan da aka dauka. (Lubabatu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China