2020-02-28 16:16:35 cri |
Bisa alkaluman kididdigar da ma'aikatar kula da cututtuka ta kasar Koriya ta Kudu ta bayar a yau Jumma'a, daga karfe hudu na yammacin jiya zuwa karfe tara na safiyar yau, an kara samun mutane 256 wadanda suka kamu da cutar numfashi ta COVID-19, al'amarin da ya sa jimillar mutanen da suka kamu da cutar ta karu zuwa 2022 a kasar.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China