2020-01-30 21:55:11 cri |
Sharhin ya nuna cewa, maida moriyar al'umma a gaban kome da kuma dogara ga karfin jama'a kyakkyawar al'ada ce ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shi ne dalilin da ya sa kasar ta iya samun ci gaba da tsayawa. Kalaman Xi Jinping na nuna wajibci gami da muhimmancin karfafawa daukacin al'ummar kasar gwiwar su shiga a dama da su a ayyukan dakile yaduwar cutar.
Hannu daya ba ya daukar jinka, a cewar malam Bahaushe. A halin yanzu al'ummar kasar Sin sun zama tsintsiya madaurinki guda domin daukar matakan kandagarkin yaduwar wannan cuta. Dukkanin larduna 31 a kasar sun kaddamar da matakan koli domin tinkarar annobar cutar, domin ba da fifiko ga aikin dakile yaduwar cutar. Sa'an nan jami'an gwamnati a matakai daban-daban sun shiga wurare daban-daban domin daukar matakan hana yaduwar cutar, kana ma'aikatan jinya sama da dubu shida sun tafi lardin Hubei domin ba da tallafin gaggawa. Ma'aikata daga sana'o'i daban-daban na himmatuwa wajen samar da kayan bukatun gaggawa ba dare ba rana, masana kimiyya da fasaha su ma suna kokarin nazarin allurar rigakafin wannan cuta. Wannan ya nuna cewa, al'ummar kasar daga bangarori daban-daban na bakin kokarinsu wajen hana yaduwar cutar.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China