Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
UNICEF: Karuwar rikici a yankin tsakiyar Sahel na mummunan tasiri kan yara
2020-01-29 16:09:38        cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya yi gargadin cewa, karuwar rikicin masu dauke da makamai a fadin kasashen Burkina Faso da Mali da Niger, na mummunan tasiri kan rayuwar yara da samar musu ilimi da kariya da kuma ci gaba.

Rahoton da asusun ya fitar a jiya, ya ce karuwar rikici a yankin tsakiyar Sahel na Afrika, na nufin kusan yara miliyan 5 za su bukaci agajin gaggawa a bana, adadin da ya karu kwatankwacin miliyan 4.3 na 2019.

A cewar rahoton asusun, ana kai wa yara hari da sace su ko horar da su a matsayin mayakan kungiyoyin saboda karuwar rikici da rashin tsaro a Burkina Faso da Mali da Niger. Ya kara da cewa, tun daga farawar rikicin a shekarar 2019, ya tilastawa yara sama da 670,000 a fadin yankin tserewa daga gidajensu.

UNICEF na neman dala miliyan 208 domin gudanar da ayyukan da take yi a yanzu, inda take aiki da abokan huldarta a fannonin bada kariya da samar da ilimi da kiwon lafiya da abinci mai gina jiki da ruwa da tsafta. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China