Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Li Keqiang ya jagoranci taron rukunin ba da jagorancin ayyukan yaki da cutar numfashi da ta barke a kasar
2020-01-26 22:12:58        cri
A yau Lahadi 26 ga watan Janairu, Li Keqiang, firaministan kasar Sin, kana jagoran rukunin ba da jagorancin ayyukan yaki da cutar numfashi da kwayoyin cutar coronavirus ke haifarwa, ya jagoranci taron rukunin don yin nazarin yadda za'a gudanar da ayyukan rigakafi da shawo kan annobar.

Taron ya ce ya kamata kwamitocin jam'iyyar kwaminis mai mulkin kasar da gwamnatoci a dukkan matakai su kara fahimtar matsanancin halin da ake ciki game da kandagarki, da yaki da cutar, kana a mayar da batun kula da lafiyar jama'a sama da komai, da daukar kwararan matakai, da kara kaimi, da amfani da karin matakan kimiyya wajen dakile yaduwar annobar cutar.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China