Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shugabannin Masar da Rasha sun tattauna batun rikicin kasar Libya
2019-12-28 16:53:42        cri
Ofishin shugaban kasar Masar ya sanar cewa, shugaban Masar Abdel Fattah El-Sisi da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin a ranar Juma'a sun tattauna ta wayar tarho game da cigaban da aka samu dangane da batun rikicin kasar Libya.

Shugabannin biyu sun jaddada muhimmancin karfafa yin hadin gwiwa wajen warware rikicin kasar Libya, da kawar da mayakan 'yan tada kayar baya, da kungiyoyin ta'addanci, kana da batun kawo karshen yin shisshigin kasashen waje a harkokin cikin gidan Libyan, kakakin shugaban kasar Masar Bassam Radi ya bayyana cikin wata sanarwa.

Tattaunawar ta El-Sisi da Putin ta zo ne bayan da shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya bada sanarwa a ranar Alhamis cewa Turkiyya zata tura dakaru zuwa kasar Libya bisa ga bukatar da gwamnatin Libyan wacce MDD ta amince da ita ta nema nan da wata mai zuwa.

Masar ta nuna damuwa game da kan iyakar kasar mai tazarar kilomita 1,200 da Libya dake yammacin kasar inda mayaka da masu fasa kwaurin makamai ke cin karensu babu babbaka tun daga shekarar 2011.

A ranar 11 ga watan Disamba, El-Sisi ya sanar da cewa za'a kaddamar da cikakken shirin warware rikicin Libya nan da wasu watanni masu zuwa.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China