![]() |
|
2019-11-16 16:31:48 cri |
Jahohin dake shiyyar tsakiyar Najeriya sun sha fuskantar mummunar ambaliyar ruwa tun daga watan Augasta, sakamakon mamakon ruwan sama da aka sheka, gami da iska mai karfi, da kuma tumbatsar koguna da tafkuna.
Allu Maga, shugaban hukumar bada agajin gaggawa na jahar Nasarawa ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, dubban mutane ne suka kauracewa muhallansu da kuma hasarar dukiya ta miliyoyin nairori.
A cewar jami'in, al'ummomin da lamarin ya shafa sun hada da mutanen dake zaune a gabar tekun Benue. Ya kara da cewa, tun da farko an yi wa al'ummomin dake zaune a wadannan yankunan gargadin yiwuwar fuskantar ambaliyar ruwa amma suka yi biris tare da yin ikirarin cewa filayen dake yankunan sun gada ne daga iyaye da kakaninsu.
Maga yace, tuni gwamnatin jahar ta fara rabon kayayyakin tallafi ga mutanen da iftila'in ya shafa.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China