Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Rahoto: FDI na kasar Sin ya karu da kashi 4 a watanni 6 duk da takaddamar kasuwanci
2019-10-30 10:45:25        cri

Wani rahoton taron kasuwanci da bunkasa cigaba na MDD (UNCTAD) ya wallafa ya nuna cewa, duk da irin takaddamar cinikin da kasar Sin ke fuskanta, kasar ta samu karuwar ma'aunin tattalin arzikinta na jarin kai tsaye na kasashen ketare wato (FDI), inda ya karu da kashi 4% a watanni shidan farko na shekarar 2019 adadin ya kai dala biliyan 73.

A cewar kididdigar baya bayan nan ta cibiyar dake sanya ido kan zuba jari ta kasa da kasa, baki dayan alkaluman FDI na duniya a watanni shidan farko na bana ya tasamma dala biliyan 640, inda ya karu da kashi 24%, ya zarta dala biliyan 517 na makamancin lokacin shekarar 2018, a daidai lokacin da tsarin sauye sauyen biyan harajin Amurka ya fara sanya wasu rukunin kamfanonin kasar Amurkar ke neman dawo da kudinsu gida.

Sai dai duk da takaddamar cinikayyar, har yanzu kasar Sin tana matsayi na biyu mafi karfin jarin na FDI a duniya. Amurka har yanzu ita ce ta farko mafi karfin jarin FDI wanda ya tasamma dala biliyan 143.

UNCTAD ta ce, hasashen da aka yi na shekarar nan baki daya yana nan bai sauya ba, kamar yadda aka yi hasashen tunda farko adadin zai karu zuwa kashi 5-10%. Sai dai kuma, koma bayan tattalin arzikin duniya da kuma yakin cinikin dake cigaba da faruwa zai iya zama babbar barazana ga karuwar tattalin arzikin na FDI. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China