2019-10-26 15:55:56 cri |
Stephane Dujarric, ya ce ayyukan ta'addanci ya kara yawaita adadin mutanen da suke barin gidajensu a jihar Borno, inda a bana kadai, mutane sama da 140,000 suka bar gidajensu. Ya na mai cewa galibin manoma sun yi asarar lokutan noma, kuma sama da mutane miliyan 3 na fuskantar rashin abinci.
Ya kara da cewa, tun farkon barkewar rikicin, MDD da abokan huldarta ke taimakawa wajen aiwatar da ayyukan jin kai a arewa maso gabashin Nijeriya, yana mai cewa, a 2019 kadai, sun samar da kayyakin ceton rai ga sama da mutane miliyan 3.8.
Sai dai, Stephane Dujarric ya ce yanzu haka, sama da mutane miliyan 7 suna bukatar taimakon jin kai a jihohin Borno da Adamawa da Yobe. (Fa'iza Mustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China