2019-10-24 20:36:06 cri |
Jami'in wanda ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai Maiduguri, babban birnin jihar Borno, ya ce, an samu wannan nasara ce, sakamakon matakan da sojoji ke dauka a yankin. Hakan a cewarsa, ya biyo bayan matakan da gwamnatin Najeriya da sojoji da kungiyoyin bayar da agaji ke dauka, don kawo karshen kuncin da jama'a suka dade suna fama da shi, sakamakon ayyukan ta'addanci na mayakan Boko Haram. (Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China