
A wannan mako, za ku ji wata hira da wakilinmu Ahmad Fagam ya yi da Alhaji Lawal Alhassan darakta janar na hukumar janyo masu zuba jari a jihar Kano dake tarayyar Najeriya, wanda ya taba kawo ziyarar aiki kasar Sin domin neman janyo hankalin kamfanonin kasar Sin don su zuba jarinsu a jihar Kano, ya bayyana muhimmancin dangantakar dake tsakanin kasar da jihar Kano da ma Najeriya baki daya. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance da Alhaji Lawal Alhassan.(Murtala Zhang)