Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kwalejojin kasar Sin na da malamai 28,000 masu koyar da kirkire-kirkire da kasuwanci
2019-10-11 10:59:37        cri
Ma'aikatar ilimi ta kasar Sin, ta ce kasar na da kimanin malamai 28,000 dake koyar da kirkire-kirkire da kasuwanci, da wasu malaman na wucin gadi 93,000, a kwalejoji da jami'o'in kasar.

Yayin wani taron manema labarai, shugaban sashen kula da ilimin gaba da sakandare na ma'aikatar, Wu Yan, ya ce hukumar kula da harkokin kudi ta kasar Sin, ta ware yuan miliyan 889, kwatankwacin dala miliyan 124, domin gina cibiyoyin bada horo a kwalejoji da jami'o'in kasar 19, da nufin inganta gyare-gyare a fannin bada ilimin kasuwanci da kirkire kirkire.

Ya ce yanzu haka, akwai kwasakwasai 28,000 na kirkire kirkire da kasuwanci na intanet da wadanda ba na intanta ba, a fadin kasar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China