Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin za ta sanya karin wasu albarkatun gona cikin jerin hajoji da za a cirewa karin haraji
2019-09-13 20:13:51        cri
Ofishin hukumar kwastam na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya sha alwashin sanya karin wasu albarkatun gona da ake shigowa da su Sin daga Amurka, cikin jerin hajoji da za a cirewa karin haraji.

A wani ci gaban kuma, mahukuntan kasar ta Sin sun nuna goyon baya ga wasu kamfanonin Sin, wadanda ke fatan sayo wasu albarkatun gona daga Amurka, bisa tanajin kasuwanni, da kuma tsarin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kamar dai yadda wata majiya daga hukumar tsara ci gaba da aiwatar da sauye sauye ta kasar, da ma'aikatar cinikayyar kasar suka bayyana.

Wannan mataki dai na zuwa ne, bayan da Amurka ta yanke shawarar yin wasu sauye sauye, game da harajin da ta ayyana karawa kan hajojin Sin dake shiga kasar, tun daga ranar 1 ga watan Oktoba mai zuwa. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China