Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Afrika ta kudu ta ayyana watan kiyaye rayuwar 'yan sandan kasar daga ayyukan bata gari
2019-09-02 10:57:34        cri
Gwamnatin kasar Afrika ta kudu ta ayyana watan Satumba a matsayin watan kiyaye rayuwar 'yan sandan kasar a yayin da ake samu karuwar jami'an 'yan sandan kasar dake fadawa cikin garari a sanadiyyar karuwar ayyukan bata gari.

Mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu David Mabuza yace, a cikin wannan watan, ya kamata a yayata sakonnin muhimmancin lafiyar 'yan sanda a dukkan lungu da sako na kasar.

A cewar Mabuza, manufar shirya gangamin shine, domin fadakar da al'umma muhimmancin yin hadin gwiwa tsakanin jami'an 'yan sanda da al'ummar kasar.

Yace a lokacin bikin tunawa da ranar 'yan sanda ta kasar Afrika ta kudu, wajibi ne a fahimci cewa hadin gwiwa tsakanin 'yan sanda da jama'a yana bukatar a karfafashi kuma dukkan 'yan kasa su tallafawa shirin.

Mabuza ya jaddada aniyar yin aiki tare da ministan 'yan sandan kasar Bheki Cele da nufin kakkabe ayyukan bata gari a fadin kasar.

Yace ta hanayar cikakken hadi gwiwa tsakanin 'yan sanda da al'ummar kasa ne za'a iya cimma nasarar samun zaman lafiya, da bin doka da oda, kana za'a kawo karshen yawan kashe jami'an 'yan sandan kasar.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China