2019-08-27 11:02:23 cri |
Tun da farko a wannan rana, Netanyahu ya baiwa ofishinsa umarnin shirin gina sabbin matsugunan Yahudawa kimanin 300 a yankin Dolev, kusa da birnin Ramallah na al'ummar Falasdinawa wanda Yahudawa suka mamaye a yammacin kogin Jordan.
Netanyahu ya ce, an dauki wannan mataki ne domin ramuwar gayya kan mummunan harin bam da Falastinawa suka kaddamar a ranar Juma'a, wanda ya yi sanadiyyar hallaka wata yarinya bayahudiya 'yar shekaru 17 da haihuwa, kana da raunata dan uwanta da mahaifin yarinyar.
Domin mayar da martani, Hanan Ashrawi, mamban kwamitin gudanarwar kungiyar fafutukar ceto al'ummar Falastinawa, ya bayyana matakin da mista Netanyahu ya dauka a lokacin taron manema labarai da cewa, wauta ne da neman tada rikici ta hanyar nuna cin zali. (Ahmad Fagam)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China