2019-08-12 10:58:33 cri |
Yanzu haka lokaci ne da daliban jami'o'in da dama suka kammala karatunsu suke kuma neman aikin yi. Shugabar sashen kula da samar da guraben aikin yi ta ma'aikatar kwadago da ba da tabbaci ga al'umma, Madam Zhang Ying ta bayyana cewa, yawan daliban da suka kammala karatu a jami'o'in kasar Sin a wannan shekara ya kai miliyan 8 da dubu 340, kuma yanzu haka ana samar musu da guraben aiki yadda ya kamata. Nan gaba kadan, ma'aikatar za ta gudanar da ayyuka a fannoni da dama, don taimaka musu wajen samun guraben ayyuka.(Lubabatu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China