Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jakadan Sin dake Nijeriya ya yi bayani game da batun yankin Hong Kong
2019-08-10 20:43:11        cri

Jakadan Sin dake kasar Nijeriya Zhou Pingjian ya yi tsokaci kan batun yankin Hong Kong ga gidan rediyon kasar Nijeriya cewa, yankin Hong Kong yana fuskantar mawuyacin hali bayan da ya koma babban yankin kasar Sin. Aikin dake gaban koma a yankin Hong Kong shi ne kawo karshen rikicin dake faruwa da maido da odar yankin.

Zhou Pingjian ya yi nuni da cewa, tsananta halin da ake ciki a yankin Hong Kong yana da nasaba da wasu 'yan siyasa na kasashen yammacin duniya musamman na kasar Amurka, wadanda suka zuga jama'ar yankin, wadanda suka nuna goyon baya ga masu tsattauran ra'ayi da masu tada rikici, manufarsu ita ce nuna adawa ga kasar Sin ta hanyar tada rikici a yankin Hong Kong.

Zhou Pingjian ya jaddada cewa, gwamnatin kasar Sin ba ta amince wasu kasashe su tsoma baki kan harkokin yankin Hong Kong, da kuma tada rikici a yankin ba. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China