![]() |
|
2019-08-09 10:58:35 cri |
Kaza lika kafar watsa labarai ta kasar ENA, ta rawaito Arayaselassie na cewa, layin dogo mai aiki da lantarki da kasar Sin ta gudanar, aka kuma kaddamar a watan Janairun shekarar 2018, wanda ya hada kasar Habasha da Djibouti, ya taimaka matuka wajen bunkasa damar Habasha ta fitar da hajojin ta zuwa kasuwannin ketare. Hakan ya samu ne sakamakon damar fitar da sundukan dakon kaya cikin sauri daga yankin masana'antun kasar dake babban yankin Habasha, zuwa tashar jiragen ruwa dake Djibouti.
Jami'ar ta kara da cewa, dunbin kudaden da kasar Habashan ta samu a tsakanin shekarar 2018 zuwa 2019, sun haura na shekarar 2017 zuwa 2018 da kusan kaso 50 bisa dari. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China