2019-08-06 14:05:39 cri |
Mr. Mwiya ya godewa kungiyar SADC mai kasashe mambobi 16, bisa amincewar ta ga muhimmancin sassa masu zaman kan su, a matsayi bangare mai tasiri ga ci gaban hada hadar zuba jari, da samar da ci gaba.
A nasa tsokaci, sabon jagoran majalissar, kuma shugaban asusun sassa masu zaman kan su a Tanzania ko TPSF a takaice Salum Shamte, cewa ya yi, abu ne da ya wajaba, sassan gwamnati da na masu zaman kan su, su yi hadin gwiwa don magance kalubalen dake haifar da koma baya ga nahiyar Afirka.
A shekarar 1992 ne aka kafa kungiyar SADC, kungiyar da ta mayar da hankali ga hade sassan kudancin Afirka wuri guda, da yaki da talauci, ta hanyoyin bunkasa tattalin arziki, da wanzar da zaman lafiya da tsaro. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China