2019-08-06 09:36:46 cri |
Jami'an tsaro dauke da kayan aiki sun bazu a sassan kasar, inda suka tsaurara tsaro a yankunan da ake fargabar masu zanga zangar zasu yi gangami, tsohon dan takarar neman shugabancin kasar ne yayi yunkurin shirya zanga zangar.
A martanin data mayar, gwamnatin Najeriya tace hanyar kadai da ake bi wajen sauya gwamnati a tsarin mulkin demokaradiyya shi ne ta hanyar zabe.
Cikin sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa Garba Shehu, ya bayyana cewa, a koda yaushe gwamnati tana maraba da 'yan kasa su gudanar da zanga zangar lumana domin bayyana bacin ransu ga gwamnati, amma a cewarsa zanga zangar lumana ta sha bamban da yunkurin kifar da gwamnati.
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China