![]() |
|
2019-07-19 09:37:21 cri |
Wu ya bayyana hakan ne yayin taron kwamitin sulhun MDD game da karfafa alaka ta yadda irin wadannan kasashe za su samu nasarar farfado da kansu.
Ya ce, kasashe da dama sun fara aiwatar da matakan raya kansu, da na tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwa na dogon lokaci, bayan kawo karshen tashin hankalin da suka fuskanta.
Jami'in na kasar Sin ya ce, ya kamata MDD da kasa da kasa su baiwa irin wadannan kasashe taimako da goyon bayan da ya dace.
Wu Haitao ya kuma jaddada muhimmancin yin hadin gwiwa, yana mai cewa ya kamata MDD da ilahirin al'ummomin kasa da kasa, dake taimakawa kasashe wajen farfadowa bayan tashin hankali, su karfafa sadarwa da hada kai da kungiyoyin yankuna da na shiyya, su kuma sakarwa kungiyoyin tarayyar Afirka, da kasashen Larabawa da ASEAN da sauransu, ta yadda za su taka rawar da ta dace a harkokin shiyya-shiyya.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China