Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Raya yankin cinikayya cikin 'yanci na Afirka zai samar da kuzarin kiyaye ra'ayin bangarori da dama da yin cinikayya cikin 'yanci
2019-07-08 20:58:10        cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Litinin, cewa a yanayin da duniya ke ciki na rashin zaman karko da tabbas, soma raya yankin cinikayya maras shinge a Afirka zai kara samar da kuzari ga kokarin da ake na kiyaye ra'ayin bangarori da dama, da gudanar da cinikayya cikin 'yanci da kuma raya tattalin arzikin duniya mai salon bude ga kowa.

A jiya ne aka bude taron kolin kungiyar kasashen tarayyar Afirka (AU) a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijer, inda aka sanar da fara aiki da yankin cinikayya cikin 'yanci na babbar nahiyar Afirka. Game da wannan batu Geng ya ce, a cikin shekaru kusan 10 da suka gabata, kasar Sin ta yi ta kasance abokiyar cinikayya mafi girma ta kasashen Afirka, ta kuma dauki matakai masu yakini a fannonin hada sassan kayayyakin more rayuwa da samar da saukin cinikayya, inganta masana'antu da dai sauransu, kana ta tsaya tsayin daka wajen goyon baya kasashen Afirka da su raya kasashensu bisa karfin kansu, da raya yankin cinikayya cikin 'yanci. Geng ya kara da cewa, fara aiki da yankin cinikayya cikin 'yanci na nahiyar Afirka ya bude wata sabuwar makoma ga hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Bilkisu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China